Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Kid 3:1-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Waɗannan su ne zuriyar Haruna da Musa lokacin da Ubangiji ya yi magana da Musa a bisa Dutsen Sinai.

2. Waɗannan su ne sunayen 'ya'yan Haruna, maza, Nadab ɗan fari, da Abihu, da Ele'azara, da Itamar.

3. Waɗannan su ne sunayen 'ya'yan Haruna, maza, da aka naɗa firistoci domin su yi aikin firist.

4. Amma Nadab da Abihu sun mutu a gaban Ubangiji a jejin Sinai, a sa'ad da suka ƙona turare da haramtacciyar wuta. Sun mutu, ba su da 'ya'ya, saboda haka Ele'azara da Itamar suka yi aikin firist su kaɗai a zamanin mahaifinsu Haruna.

5. Ubangiji ya ce wa Musa,

6. “Kawo kabilar Lawiyawa kusa, ka sa su su yi aiki tare da Haruna, firist.

7. Sai su yi wa firistoci da dukan jama'a aiki a gaban alfarwa ta sujada.

8. Su za su lura da kayayyakin alfarwa ta sujada su kuma yi wa Isra'ilawa aiki.

9. Abin da Lawiyawa za su yi, shi ne su yi wa Haruna da 'ya'yansa aiki.

10. Ka sa Haruna da 'ya'yansa maza, su kula da aikinsu na firist, idan kuwa wani mutum dabam ya yi ƙoƙarin yin wannan aiki, to, za a kashe shi.”

11. Ubangiji kuma ya ce wa Musa,

Karanta cikakken babi L. Kid 3