Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Kid 25:7-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Finehas ɗan Ele'azara, wato jikan Haruna, firist, ya gani, sai ya tashi daga cikin taron, ya ɗauki mashi.

8. Ya bi Ba'isra'ilen, har zuwa ƙuryar alfarwar, ya soke dukansu biyu, Ba'isra'ilen da macen, har ya sha zarar macen. Da haka aka tsai da annoba daga Isra'ilawa.

9. Duk da haka annobar ta kashe mutane dubu ashirin da dubu huɗu (24,000).

10. Sai Ubangiji ya ce wa Musa,

11. “Finehas ɗan Ele'azara, wato jikan Haruna, firist, ya kawar da fushina daga Isra'ilawa saboda ya yi kishi irin nawa a gabansu, don haka ban shafe Isra'ilawa saboda kishina ba.

12. Domin haka ina yi masa alkawarin da ba zai ƙare ba.

13. Alkawarin zai zama nasa da na zuriyarsa, wato alkawarin zama firist din din din, domin ya yi kishi saboda Allahnsa. Ya kuwa yi kafara domin Isra'ilawa.”

14. Sunan Ba'isra'ilen da aka kashe tare da Bamadayaniyar, Zimri ɗan Salu, shi ne shugaban gidan Saminawa.

15. Sunan Bamadayaniya kuwa, Kozbi, 'yar Zur. Shi ne shugaban mutanen gidan ubansa a Madayana.

Karanta cikakken babi L. Kid 25