Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Kid 20:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sai dukan taron jama'ar Isra'ilawa suka zo jejin Zin a watan fari, suka sauka a Kadesh. A nan ne Maryamu ta rasu, a nan kuma aka binne ta.

2. Da jama'a suka rasa ruwa, sai suka taru suka tayar wa Musa da Haruna.

3. Suka ce wa Musa, “Da ma mun mutu kamar yadda 'yan'uwanmu suka mutu a gaban Ubangiji.

4. Don me ka fito da taron jama'ar Ubangiji zuwa cikin wannan jeji don mu mutu a nan, mu da dabbobinmu?

5. Don me kuma ka sa muka fito daga masar, ka kawo mu a wannan mugun wuri inda babu hatsi, ko ɓaure, ko inabi, ko rumman, ko ruwan da za a sha ma?”

Karanta cikakken babi L. Kid 20