Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Josh 6:23-27 Littafi Mai Tsarki (HAU)

23. Sai samarin da suka leƙo asirin ƙasar suka shiga, suka fito da Rahab, da mahaifinta, da mahaifiyarta, da 'yan'uwanta, da dukan waɗanda suke nata, suka fito da dukan danginta, suka saukar da su a bayan zangon Isra'ilawa.

24. Suka ƙone birnin da wuta da dukan abin da yake a cikinsa, sai dai azurfa, da zinariya, da kwanonin tagulla, da na baƙin ƙarfe ne, suka ajiye a cikin taskar masujadar Ubangiji.

25. Amma Joshuwa ya bar Rahab da rai, da ita da iyalin mahaifinta, da dukan waɗanda suke nata. Rahab ta yi zamanta wurin Isra'ilawa har wa yau domin ta ɓoye manzannin da Joshuwa ya aika don su leƙo asirin Yariko.

26. A lokacin nan Joshuwa ya yi musu magana da rantsuwa ya ce,“La'ananne ne mutum a gaban UbangijiWanda ya tashi don ya sāke gina birnin nan Yariko.A bakin ɗan farinsa zai kafa tushensa,A bakin autansa kuma zai gina ƙofofinsa.”

27. Ubangiji yana tare da Joshuwa, ya kuwa yi suna cikin dukan ƙasar.

Karanta cikakken babi Josh 6