10. Ku mutanen Urushalima, ku fita daga cikin birni,Ku gyara hanyoyi domin jama'arku da suke komowa!Ku shirya babbar hanya,Ku kawar da duwatsu daga hanyar!Ku sa alama domin al'ummai su sani,
11. Ubangiji yana sanarwa ga dukan duniya,Cewa, “Ku ce wa jama'ar Urushalima,Ubangiji Mai Cetonku yana zuwa,Yana kawo mutanen da ya cece su.”
12. Za a ce da ku, “Tsattsarkar Jama'ar Allah,”“Jama'ar da Ubangiji ya Fansa!”Za a kira Urushalima, “Birnin da Allah yake Ƙauna,”“Birnin da Allah bai Yashe shi Ba.”