Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 60:16-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. Al'ummai da sarakuna za su lura da keKamar yadda uwa take lura da ɗanta.Za ki sani, ni Ubangiji, na cece ki,Allah Mai Iko Dukka na Isra'ila ya fanshe ki.

17. “Zan kawo miki zinariya maimakon tagulla,Azurfa maimakon baƙin ƙarfe,Tagulla kuma maimakon itace.Za ki sami baƙin ƙarfe maimakon dutse.Masu mulkinki ba za ƙara zaluntarki ba,Zan sa su yi mulki da gaskiya da salama.

18. Ba za a ƙara jin hayaniyar tashin hankali ba,Ba za a ƙara aukar wa ƙasar da ɓarna ba.Zan kiyaye ki, in kāre ki kamar garu,Za ki yi yabona domin na cece ki.

Karanta cikakken babi Ish 60