Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 49:10-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Ba za su taɓa jin yunwa ko ƙishi ba.Ba za su sha zafin rana da na hamada ba,Gama wanda yake ƙaunarsu ne zai bi da su.Zai bi da su zuwa maɓuɓɓugan ruwa.

11. “Zan yi babbar hanya ta kan duwatsu,In kuma shirya hanya domin mutanena su bi.

12. Mutanena za su zo daga can nesa,Daga Birnin Sin a kudu,Daga yamma, da arewa.”

13. Ku raira, ku sammai! Ki yi sowar murna, ke duniya!Bari duwatsu su ɓarke da waƙa!Ubangiji zai ta'azantar da mutanensa,Zai ji juyayin mutanensa da suke shan wahala.

14. Amma mutanen Urushalima suka ce,“Ubangiji ya yashe mu!Ya manta da mu.”

15. Saboda haka Ubangiji ya amsa ya ce,“Mace za ta iya mantawa da jaririnta,Ta kuma ƙi ƙaunar ɗan da ta haifa?Ya yiwu mace ta manta da ɗanta,To, ni ba zan taɓa mantawa da ku ba.

16. Ya Urushalima, ba zan taɓa mantawa da ke ba,Na rubuta sunanki a gabana.

17. “Su waɗanda za su sāke gina ki suna tafe yanzu,Waɗanda suka lalatar da ke kuwa za su tashi.

18. Ki dudduba, ki ɗaga idonki, ki ga abin da yake faruwa!Mutanenki suna tattaruwa suna komowa gida!Hakika, da yake ni ne Allah Mai Rai,Za ki yi fāriya da mutanenki,Kamar yadda amarya take fāriya da kayan adonta!

19. “Aka lalatar da ƙasar, ta zama kufai,Amma yanzu za ta yi wa waɗanda suke komowa domin su zauna cikinta kaɗan.Waɗanda suka lalatar da ke kuwa,Za a kawar da su daga gare ki.

20. Mutanenki da aka haifa a lokacin zaman talala,Wata rana za su ce miki,‘Wannan ƙasa ta yi kaɗan ƙwarai,Muna bukatar ƙarin wurin zama!’

Karanta cikakken babi Ish 49