Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 48:5-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Tuntuni na yi faɗi a kan makomarku,Na hurta abubuwa tun kafin su faru,Domin kada ku ɗauka cewa gumakanku ne suka yi su,Siffofinku ne kuma suka sa abin ya zama haka.

6. “Dukan abin da na faɗa yana cika yanzu,Sai ku yarda, faɗata gaskiya ce.Yanzu zan faɗa muku sababbin abubuwan da za su zo,Abubuwan da ban bayyana su a dā ba.

7. Yanzu ne kaɗai nake sawa su faru,Ba wani abu makamancin wannan da ya faru a baya.Da ya faru, da za ku ɗauka cewa kun san kome a kansa.

8. Na sani ba za a iya gaskata ku ba,Tun daga haihuwarku kuma an san ku da tayarwa.Shi ya sa ba ku taɓa jin wannan ba ko kaɗan,Ko kalma ɗaya ba ta taɓa shiga kunnenku ba.

9. “Saboda mutane su yi yabon sunanaShi ya sa nake danne fushina,Ina kuma ɓoye shi, kada in hallaka ku.

10. Na gwada ku da wutar wahala,Kamar yadda ake tace azurfa a tanda,Amma na tarar ba ku da amfani.

11. Abin da na yi, na yi shi don kaina ne,Ba zan bari a rasa girmama sunana ba,Ko kuwa wani dabam ya sami ɗaukakaWadda take tawa ce, ni kaɗai.”

12. “Ku kasa kunne gare ni, ya Isra'ila, jama'ar da na kira!Ni ne Allah, farko, da ƙarshe, Allah Makaɗaici!

13. Dantsena ne ya kafa harsashin ginin duniya,Ya kuma shimfiɗa sammai.Lokacin da na kira duniya da sararin sama,Sukan zo nan da nan, su gabatar da kansu!

14. “Ku tattaru, ku duka, ku kasa kunne!Ba ko ɗaya cikin alloli da zai iya yin annabci ba,Cewa mutumin da na zaɓa, shi zai iya fāɗa wa Babila,Zai yi abin da na umarce shi.

15. Ni ne na yi magana, na kuwa kira shi,Na yi masa jagora na kuwa ba shi nasara.

16. “Yanzu fa, sai ku matso kusa da ni,Ku ji abin da nake faɗa.Tun da farko na yi magana da ku a fili,A koyaushe nakan cika maganata.”(Yanzu Ubangiji Allah ya ba ni iko, ya kuwa aike ni.)

17. Allah Mai Tsarki na Isra'ila,Ubangiji, wanda ya fanshe ku, ya ce,“Ni ne Ubangiji Allahnku,Wanda yake so ya koya muku domin amfanin kanku,Ya kuwa nuna muku hanyar da za ku bi.

Karanta cikakken babi Ish 48