Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 45:5-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. “Ni ne Ubangiji, ba wani Allah sai ni.Zan ba ka irin ƙarfin da kake bukata,Ko da yake kai ba ka san ni ba.

6. Na yi wannan domin dukan waɗanda suke daga wannan bangon duniya zuwa wancanSu sani ni ne Ubangiji,Ba kuwa wani Allah sai ni.

7. Ni na halicci haske duk da duhu,Ni ne na kawo albarka duk da la'ana.Ni Ubangiji, na yi dukkan waɗannan abu.

8. Zan aiko da nasara daga sararin sama kamar ruwan sama.Ƙasa za ta buɗe ta karɓe ta,Za ta kuwa hudo da 'yanci da gaskiya.Ni Ubangiji, ni zan sa haka ya faru.”

9. Ko tukunyar yumɓu tana iya gardama da magininta,Tukunyar da take daidai da sauran tukwane?Ko yumɓu ya iya tambayar abin da maginin yake yi?Ko tukunya tana iya gunaguni a kan magininta?

10. Ko akwai wanda zai iya ce wa iyayensa,“Don me kuka haife ni kamar haka?”

Karanta cikakken babi Ish 45