Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 44:3-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. “Zan ba da ruwa ga ƙasa mai ƙishi,In kuma sa rafuffuka su yi gudu a hamada.Zan kwararo da albarka a kan 'ya'yanku,In sa albarkata kuma a kan zuriyarku.

4. Za su yi kumari kamar ciyawar da ta sami ruwa sosai,Kamar itatuwan wardi a gefen rafuffukan ruwa mai gudu.

5. “Da ɗaya ɗaya da ɗaya ɗaya mutane za su ce, ‘Ni na Ubangiji ne!’Za su zo su haɗa kai da jama'ar Isra'ila.Ko wanne zai ɗaura sunan Ubangiji a dantsensa,Ya ce da kansa ɗaya daga cikin mutanen Allah.”

6. Ubangiji, wanda yake mulkin Isra'ila, ya kuma fanshe su,Ubangiji Mai Runduna, yake faɗar wannan,“Ni ne farko, da ƙarshe, Allah Makaɗaici,Ba wani Allah sai ni.

7. Ko akwai wanda zai iya yin abin da na yi,Ya kuma fito fili ya faɗi abin da zai faruTun daga farko, har zuwa ƙarshe?

8. Ya jama'ata, kada ku ji tsoro!Kun sani tun daga zamanin dā can, har zuwa yanzu,Na faɗa tun da wuri abin da zai faru.Ku ne kuwa shaiduna!Ko akwai wani Allah?Ko akwai wani Allah mai iko da ban taɓa jin labarinsa ba?”

9. Dukan waɗanda suke ƙera gumaka mutanen banza ne, gumakan da suke sa wa kuɗi da tsada kuma aikin banza ne. Waɗanda suke yi wa gumaka sujada kuwa makafi ne su, jahilai, za su sha kunya.

10. Wannan aikin banza ne, mutum ya yi siffa da ƙarfe don ya yi mata sujada!

Karanta cikakken babi Ish 44