Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 42:22-25 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22. Amma yanzu an washe mutanensa,Aka kukkulle su a kurkuku,Aka ɓoye su a rami.Aka yi musu fashi, aka washe su,Ba wanda ya zo domin ya kuɓutar da su.

23. Ko akwai wanda zai kasa kunne ga wannan?Ko za ku kasa kunne ku yi lura daga yanzu?

24. Wane ne ya ba da Isra'ila ga masu waso?Ubangiji ne kansa, shi wanda muka yi wa zunubi!Ba mu iya zama kamar yadda yake so mu yi ba,Ko mu yi biyayya da koyarwarsa da ya ba mu.

25. Domin haka ya sa mu ji zafin fushinsa,Mu kuma sha wahalar da yaƙi ya kawo.Fushinsa ya yi ƙuna cikin dukan Isra'ila kamar wuta,Amma ba mu taɓa sanin abin da yake faruwa ba,Ba mu koyi kome daga wannan ba ko kaɗan.

Karanta cikakken babi Ish 42