Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 41:2-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. “Wane ne wannan da ya kawo mai yin nasara daga gabas,Ya kuma sa ya ci nasara a dukan inda ya tafi?Wa ya ba shi nasara a kan sarakuna da al'ummai?Takobinsa ya sassare su sun zama kamar ƙura!Kibansa sun warwatsar da su kamar ƙaiƙayi a gaban iska!

3. Yana biye da kora, yana kuma tafiya lafiya,Da sauri ƙwarai, da ƙyar yake taɓa ƙasa!

4. Wane ne ya sa wannan ya faru?Wane ne ya ƙudurta labarun tarihi?Ni Ubangiji, ina can tun da farko,Ni kuma Ubangiji Allah,Zan kasance a can har ƙarshe.

5. “Mutanen manisantan ƙasashe suka ga abin da na yi,Suka tsorata, suka yi rawar jiki saboda tsoro.Saboda haka duka suka tattaru wuri guda.

6. Masu aikin hannu suka taimaka suka ƙarfafa juna.

Karanta cikakken babi Ish 41