Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 41:17-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. “Sa'ad da jama'ata ta bukaci ruwa,Sa'ad da maƙogwaronsu ya bushe da ƙishi,Sa'an nan ni Ubangiji, zan amsa addu'arsu,Ni Allah na Isra'ila, ba zan taɓa yashe su ba.

18. Zan sa kogunan ruwa su yi gudu daga ƙeƙasassun tuddai,Maɓuɓɓugan ruwa su yi gudu a kwaruruka.Zan sa hamada ta zama kududdufan ruwa,Busasshiyar ƙasa kuma ta zama maɓuɓɓugan ruwa.

19. Zan sa itatuwan al'ul su tsiro a hamada,Da itacen ƙirya, da itacen ci-zaki, da zaitun.Ƙeƙasasshiyar ƙasa za ta zama kurmi,Jejin itatuwan fir.

Karanta cikakken babi Ish 41