Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 24:8-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. kaɗe-kaɗen garayunsu da gangunansu na farin ciki sun ƙare.

9. Babu sauran waƙar farin ciki ga mashayan ruwan inabi, ba kuma wanda zai ƙara jin daɗin ɗanɗanar ruwan inabi.

10. A cikin birni kome ya birkice, an kulle kowane gida don a hana mutane shiga.

11. Mutane za su tsaya a tituna, suna ihu, suna neman ruwan inabi. Farin ciki ya ƙare har abada, ya ƙare a ƙasar.

12. Birnin ya zama kango, an farfashe ƙofofinsa.

13. Wannan shi ne abin da zai sami kowace al'umma ko'ina a duniya. Zai zama kamar ƙarshen kaka sa'ad da aka karkaɗe zaitun daga kowane itace, aka kuma gama tsinke 'ya'yan inabi daga kurangar inabi.

14. Waɗanda suka tsira za su raira waƙa don farin ciki. Waɗanda suke wajen yamma za su ba da labarin girman Allah,

15. waɗanda suke wajen gabas kuma za su yabe shi. Jama'ar da take zaune a gefen teku za su yabi Ubangiji, Allah na Isra'ila.

16. Daga manisantan wurare na duniya za mu ji waƙoƙin yabon Isra'ila, al'umma adala.Amma ba ni da sauran sa zuciya! Lalacewa nake yi! Maciya amana suna ta cin amana, cin amanarsu sai gaba gaba yake yi.

Karanta cikakken babi Ish 24