Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 24:19-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

19. Duniya za ta tsage, ta farfashe ta wage.

20. Duniya kanta za ta yi tangaɗi kamar mashayi, ta yi ta yin lau kamar rumfa a lokacin hadiri. Nauyin zunuban duniya ya rinjaye ta har ƙasa, za ta fāɗi, ba za ta ƙara tashi ba.

21. A wannan rana Ubangiji zai hukunta wa ikoki na sama, da sarakunan da suke a duniya.

22. Allah zai tattara sarakuna wuri ɗaya kamar ɗaurarru a rami, zai kulle su a kurkuku kafin lokacin da zai hukunta su ya yi.

23. Wata zai duhunta, rana ba za ta ƙara haskakawa ba, domin Ubangiji Mai Runduna yake sarauta. Zai yi mulki a Urushalima a kan Dutsen Sihiyona, shugabannin jama'a za su dubi ɗaukakarsa.

Karanta cikakken babi Ish 24