Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 50:5-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Za su tambayi hanyar Sihiyona, sa'an nan su bi ta, suna cewa, ‘Bari mu haɗa kanmu don mu yi madawwamin alkawari da Ubangiji, alkawari wanda ba za a manta da shi ba.’

6. “Mutanena sun zama kamar ɓatattuntumaki,Waɗanda makiyayansu suka bauɗarda su,Suka ɓata a cikin tsaunuka,Suna kai da kawowa daga wannandutse zuwa wancan.Sun manta da shingensu.

7. Duk waɗanda suka same su, suncinye su.Maƙiyansu suka ce, ‘Ba mu yi laifiba,’Gama sun yi wa Ubangiji laifi,wanda yake tushen gaskiya,Ubangiji wanda kakanninsu sukadogara gare shi.

8. “Ku gudu daga cikin Babila,Ku fita kuma daga cikin ƙasarKaldiyawa,Ku zama kamar bunsurai waɗandasuke ja gaban garke.

9. Ga shi, zan kuta manyan ƙasashedaga arewaSu faɗa wa Babila da yaƙi.Za su ja dāgar yaƙi gāba da ita, sucinye ta.Kibansu kamar na gwanayenmayaƙa neWaɗanda ba su komowa banza.

10. Za a washe Kaldiyawa,Waɗanda suka washe su kuwa za suƙoshi,Ni Ubangiji na faɗa.

11. “Saboda kuna murna, kuna farinciki,Ku da kuka washe gādona,Saboda kuma kuna tsalle kamarkarsana a cikin ciyawa,Kuna haniniya kamar ingarmu,

12. Domin haka za a kunyatar da Babilasosai, inda kuka fito.Za ta zama ta baya duka a cikinsauran al'umma,Za ta zama hamada, busasshiyarƙasa.

13. Saboda fushin Ubangiji, ba wandazai zauna a cikinta,Za ta zama kufai,Duk wanda ya bi ta wajen Babila, zaiji tsoro,Zai kuma yi tsaki sabodalalacewarta.

14. “Dukanku 'yan baka, ku ja dāga, kukewaye Babila,Ku harbe ta, kada ku rage kibanku,Gama ta yi wa Ubangiji zunubi.

15. Ku kewaye ta da kuwwar yaƙi!Ta ba da gari,Ginshiƙanta sun fāɗi.An rushe garunta,Gama wannan sakayya ce taUbangiji.Ku sāka mata, ku yi mata kamaryadda ta yi.

Karanta cikakken babi Irm 50