Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 5:1-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. “Ku bi titunan Urushalima ko'ina!Ku dudduba ku lura!Ku bincika kowane dandali, ku gani,Ko za ku iya samun ko mutum ɗayaMai aikata adalci, mai son gaskiya,Sai in gafarta mata.

2. Ko da yake suna cewa, ‘Na rantse daran Ubangiji,’Duk da haka rantsuwar ƙarya sukeyi.”

3. Ya Ubangiji, ashe, ba masu gaskiyakake so ba?Ka buge su, amma ba su yi nishi ba,Ka hore su, amma sun ƙi horuwa,Fuskarsu ta ƙeƙashe fiye da dutse,Sun ƙi tuba.

4. Sai na ce,“Waɗannan mutane ba su da kirki,Ba su da hankali,Ba su san hanyar Ubangiji,Ko shari'ar Allahnsu ba.

5. Zan tafi wurin manyan mutane, in yimusu magana,Gama sun san nufin Ubangiji, dashari'ar Allahnsu.”Amma dukansu sun ƙi yardaUbangiji ya mallake su,Suka ƙi yi masa biyayya.

6. Domin haka zaki daga kurmi zaikashe su,Kyarkeci kuma daga hamada zaihallaka su.Damisa tana yi wa biranensukwanto,Duk wanda ya fita daga cikinsu sai ayayyage shi,Domin laifofinsu sun yi yawa,Karkacewarsu babba ce.

7. “Don me zan gafarce ki?'Ya'yanki sun rabu da ni,Sun yi rantsuwa da gumaka,Na ciyar da su har sun ƙoshi sosai,Suka yi karuwanci, suka ɗungumazuwa gidajen karuwai,

8. Kamar ƙosassun ingarmu suke,masu jaraba,Kowa yana haniniya, yana nemanmatar maƙwabcinsa.

9. Ba zan hore su saboda waɗannanabubuwa ba?Ni Ubangiji na ce, ba zan ɗauka wakaina fansa a kan wannanal'umma ba?

10. Ku haura, ku lalatar da gonarkurangar inabinta,Amma kada ku yi mata ƙarƙaf,Ku sassare rassanta,Gama su ba na Ubangiji ba ne.

11. Gama mutanen Isra'ila da mutanenYahuzaSun zama marasa aminci a gare ni.Ni Ubangiji na faɗa.”

12. Sun yi ƙarya a kan Ubangiji,Suka ce, “Ba abin da zai yi,Ba wata masifa da za ta same mu.Ba kuwa za mu ga takobi ko yunwaba.

Karanta cikakken babi Irm 5