Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 15:3-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Zan sa musu masu hallakarwa huɗu,” in ji Ubangiji, “da takobi don kisa, da karnuka don yayyagawa, da tsuntsayen sararin sama, da dabbobin duniya don su cinye, su hallakar.

4. Zan kuma sa su zama abin banƙyama ga dukan mulkokin duniya saboda abin da Manassa ɗan Hezekiya, Sarkin Yahuza ya aikata a Urushalima.

5. “Wa zai ji tausayinki, yaUrushalima?Wa zai yi baƙin ciki dominki?Wa kuma zai ratso wurinki don yatambayi lafiyarki?

6. Ni Ubangiji na ce, kun ƙi ni, kuna takomawa da baya,Don haka na nuna ikona gāba da ku,na hallaka ku,Na gaji da jin tausayinku!

7. Na sheƙe su da abin sheƙewa aƙofofin garuruwan ƙasar.Na sa 'ya'yansu su mutu, na hallakamutanena,Ba su daina yin mugayen ayyukansuba.

8. Na yawaita gwauraye, wato mata damazansu suka mutu,Fiye da yashin teku.Na kawo wa uwayen samari maihallakarwa da tsakar rana.Na sa azaba da razana su auka musufarat ɗaya.

9. Ita wadda ta haifi 'ya'ya bakwai tayi yaushi ta suma,Ranarta ta faɗi tun lokaci bai yi ba,An kunyatar da ita, an wulakantarda ita.Waɗanda suka ragu daga cikinsuZan bashe su ga takobi gaban abokangābansu.Ni Ubangiji na faɗa.”

10. Kaitona, ya mahaifiyata, da kika haife ni, mai jayayya mai gardama da kowa cikin dukan ƙasar! Ban ba da rance ba, ba kuma wanda ya ba ni rance, duk da haka dukansu suna zagina.

11. Ubangiji ya ce mini, “Zan keɓe ka domin alheri, hakika zan sa abokan gaba su yi roƙo gare ka a lokacin bala'i da kuma lokacin damuwa.

12. Wa zai iya karya ƙarfe ko tagulla daga arewa?”

13. Ubangiji ya ce mini, “Zan ba da wadatarku da dukiyarku ganima kyauta, saboda dukan zunubanku a dukan ƙasar.

14. Zan sa ku bauta wa abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, gama fushina ya kama kamar wuta, zai yi ta ci har abada.”

15. Sa'an nan Irmiya ya ce, “YaUbangiji, ka sani.Kai ne, ka ziyarce ni,Ka kuma sāka wa waɗanda suketsananta mini.Ka sani saboda kai nake shan zargi.

16. Maganarka da na samu na ci.Maganarka kuwa ta zama abarmurna a gare ni,Ta faranta mini zuciya.Gama ana kirana da sunanka,Ya Ubangiji Allah Mai Runduna.

Karanta cikakken babi Irm 15