Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Far 24:44-59 Littafi Mai Tsarki (HAU)

44. in ta amsa mini, “To, sha, zan ɗebo wa raƙumanka kuma,” bari ta zama ita ce wadda Ubangiji ya zaɓar wa ɗan maigidana.’

45. Kafin in gama tunani a zuciyata, sai ga Rifkatu ta fito ɗauke da tulun ruwa a kafaɗarta, ta gangara zuwa rijiya ta ɗebo. Na ce mata, ‘Roƙo nake, ki ba ni, in sha.’

46. Nan da nan ta sauke tulunta daga kafaɗarta, ta ce, ‘To, sha, zan kuma shayar da raƙumanka.’ Na sha, ta kuma shayar da raƙuman.

47. Na kuwa tambaye ta, ‘'Yar gidan wane ne ke?’ Ta ce, ‘Ni 'yar Betuwel ɗan Nahor, wanda Milka ta haifa masa.’ Sai na sa mata zobe a hanci, mundaye kuma a hannu.

48. Sa'an nan na yi ruku'u, na yi wa Ubangiji sujada, na yabi Ubangiji Allah na maigidana, Ibrahim, wanda ya bishe ni a hanya sosai, in auro wa ɗansa 'yar danginsa.

49. Yanzu fa, idan za ku amince ku gaskata da maigidana, ku faɗa mini, in ba haka ba, sai ku faɗa mini, domin in san abin yi, in juya dama ko hagu.”

50. Laban da Betuwel suka amsa suka ce, “Wannan al'amari daga Ubangiji ne, ba mu da iko mu ce maka i, ko a'a.

51. Ga Rifkatu nan gabanka, ka ɗauke ta ku tafi, ta zama matar ɗan maigidanka, bisa ga faɗar Ubangiji.”

52. Sa'ad da baran Ibrahim ya ji wannan, ya sunkuyar da kansa ƙasa, ya yi sujada a gaban Ubangiji.

53. Sai baran ya kawo kayan ado na azurfa, da na zinariya, da tufafi, ya bai wa Rifkatu, ya kuma ba ɗan'uwanta da mahaifiyarta kayan ado masu tsada.

54. Shi da mutanen da suke tare da shi suka ci suka sha, suka kwana wurin. Da suka tashi da safe, sai ya ce, “A sallame ni, in koma wurin maigidana.”

55. Ɗan'uwanta da mahaifiyarta suka ce, “Ka bar budurwar tare da mu har ɗan lokaci, kada ya gaza kwana goma, bayan wannan ta tafi.”

56. Amma ya ce musu, “Kada ku makarar da ni, tun da yake Allah ya arzuta tafiyata, a sallame ni domin in koma wurin maigidana.”

57. Suka ce, “Za mu kira budurwar mu tambaye ta.”

58. Suka kirawo Rifkatu suka ce mata, “Za ki tafi tare da wannan mutum?”Sai ta ce, “Zan tafi.”

59. Suka kuwa sallami Rifkatu 'yar'uwarsu da uwar goyonta, da baran Ibrahim da mutanensa.

Karanta cikakken babi Far 24