Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ezra 6:1-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sarki Dariyus kuwa ya ba da umarni a bincike ɗakin littattafai na Babila, inda aka ajiye takardun shaida.

2. Sai aka sami takarda a Ekbatana, babban lardin Mediya. A cikin takardar aka iske rubutu don tunawa.

3. “A shekara ta fari ta sarautar sarki Sairus, sai ya ba da izini a sāke gina Haikalin Allah da yake a Urushalima, wurin da za a miƙa sadaka da hadayu na ƙonawa. Sai a aza harsashi da ƙarfi. Tsayinsa zai zama kamu sittin, fāɗinsa kuwa kamu sittin.

4. Za a jera manyan duwatsu jeri uku, da jeri ɗaya na katako, a kuma biya kuɗin aikin daga baitulmalin sarki.

5. A kuma kawo kwanonin nan na zinariya da na azurfa cikin Haikalin Allah, waɗanda Nebukadnezzar ya kwaso daga cikin Haikali a Urushalima ya kawo Babila, a komar da su, a mayar da su a Haikali a Urushalima, a ajiye kowanne a wurinsa a Haikalin Allah.”

6. Sarki Dariyus ya ce, “Zuwa ga Tattenai, mai mulkin Yammacin Kogi, da Shetar-bozenai, da abokansu, wato ma'aikatan hukuma na lardin Yammacin Kogi, ku nisance su.

7. “Ku ƙyale aikin Haikalin nan na Allah kawai, ku ƙyale masu mulkin Yahudawa da dattawan Yahudawa, su sāke gina Haikalin Allah a wurin da yake a dā.

8. Ina umartarku ku biya wa dattawan Yahuza kuɗin sāke ginin Haikalin nan na Allah, a biya mutanen nan cikakken kuɗin aiki daga baitulmalin sarki, wanda yake a lardin Yammacin Kogi, ba tare da ɓata lokaci ba.

9. A ba su duk abin da suke bukata, wato kamar 'yan bijimai, da raguna, da 'yan tumaki domin yi wa Allah na Sama hadayun ƙonawa, da alkama, da gishiri, da ruwan inabi, da man naɗawa yadda firistoci a Urushalima suke bukata, sai a ba su kowace rana banda fashi,

Karanta cikakken babi Ezra 6