Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 48:29-35 Littafi Mai Tsarki (HAU)

29. Ubangiji ya ce, “Wannan ita ce hanyar da za ku raba gādo tsakanin kabilan Isra'ila. Waɗannan kuwa su ne yankunansu, ni Ubangiji Allah na faɗa.”

30. “Ƙofofin birnin a gefen arewa, kamu dubu huɗu da ɗari biyar [4,500] ne.

31. Ƙofofi uku ne, wato Ƙofar Ra'ubainu, da Ƙofar Yahuza, da Ƙofar Lawi. Ana kiran sunayen ƙofofin birnin da sunayen kabilan Isra'ila.

32. A gefen gabas, kamu dubu huɗu ne da ɗari biyar [4,500]. Ƙofofi uku ne, wato Ƙofar Yusufu, da Ƙofar Biliyaminu, da Ƙofar Dan.

33. A gefen kudu, kamu dubu huɗu da ɗari biyar [4,500]. Ƙofofi uku ne, wato Ƙofar Saminu, da Ƙofar Issaka, da Ƙofar Zabaluna.

34. A gefen yamma, kamu dubu huɗu da ɗari biyar [4,500] ne. Ƙofofi uku ne, wato Ƙofar Gad, da Ƙofar Ashiru, da Ƙofar Naftali.

35. Da'irar birnin kamu dubu goma sha takwas [18,000] ne. Daga wannan lokaci za a kira birnin, ‘Ubangiji Yana Nan!”’

Karanta cikakken babi Ez 48