Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 48:27-35 Littafi Mai Tsarki (HAU)

27. Yankin Gad yana kusa da yankin Zabaluna daga gabas zuwa yamma.

28. “Kusa da yankin Gad zuwa kudu, iyakar za ta bi ta Tamar zuwa ruwan Meriba-kadesh, sa'an nan ta bi rafin Masar zuwa Bahar Rum.”

29. Ubangiji ya ce, “Wannan ita ce hanyar da za ku raba gādo tsakanin kabilan Isra'ila. Waɗannan kuwa su ne yankunansu, ni Ubangiji Allah na faɗa.”

30. “Ƙofofin birnin a gefen arewa, kamu dubu huɗu da ɗari biyar [4,500] ne.

31. Ƙofofi uku ne, wato Ƙofar Ra'ubainu, da Ƙofar Yahuza, da Ƙofar Lawi. Ana kiran sunayen ƙofofin birnin da sunayen kabilan Isra'ila.

32. A gefen gabas, kamu dubu huɗu ne da ɗari biyar [4,500]. Ƙofofi uku ne, wato Ƙofar Yusufu, da Ƙofar Biliyaminu, da Ƙofar Dan.

33. A gefen kudu, kamu dubu huɗu da ɗari biyar [4,500]. Ƙofofi uku ne, wato Ƙofar Saminu, da Ƙofar Issaka, da Ƙofar Zabaluna.

34. A gefen yamma, kamu dubu huɗu da ɗari biyar [4,500] ne. Ƙofofi uku ne, wato Ƙofar Gad, da Ƙofar Ashiru, da Ƙofar Naftali.

35. Da'irar birnin kamu dubu goma sha takwas [18,000] ne. Daga wannan lokaci za a kira birnin, ‘Ubangiji Yana Nan!”’

Karanta cikakken babi Ez 48