23. Sa'ad da ka gama tsarkake shi, sai ka miƙa bijimi da rago marar lahani.
24. Za ka kawo su a gaban Ubangiji, firistoci za su barbaɗe su da gishiri, su miƙa su hadayar ƙonawa ga Ubangiji.
25. Kowace rana za ka riƙa miƙa akuya, da bijimi, da rago, marasa lahani domin yin hadaya don zunubi, har kwana bakwai.
26. Za su yi kafara har kwana bakwai don su tsarkake bagaden, su keɓe shi.
27. Sa'ad da suka cika kwanakin nan bakwai, sa'an nan a kan rana ta takwas zuwa gaba, firistoci za su miƙa hadayun ƙonawa da na salama a kan bagaden. Ni kuwa zan karɓe ku, ni Ubangiji Allah na faɗa.”