Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 37:18-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. Sa'ad da kuma jama'arka suka ce maka ka nuna musu abin da kake nufi da waɗannan,

19. sai ka faɗa musu, cewa ni Ubangiji Allah na ce zan karɓe sandan Yusufu, wanda yake a hannun Ifraimu da mutanen Isra'ila magoyan bayansa, in haɗa shi da sandan Yahuza in maishe su sanda guda a hannuna.

20. “Sa'ad da sandunan da ka yi rubutu a kansu suna hannunka a gabansu,

21. sai ka faɗa musu, cewa ni Ubangiji Allah na ce, zan komo da jama'ar Isra'ila daga wurin al'ummai inda suka warwatsu, zan tattaro su daga ko'ina, in maido su ƙasarsu.

Karanta cikakken babi Ez 37