Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 28:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ubangiji ya yi magana da ni ya ce,

2. “Dan mutum, ka faɗa wa Sarkin Taya, cewa Ubangiji Allah ya ce,‘Da yake zuciyarka ta cika da alfarma,Har ka ce kai allah ne,Kana zaune a mazaunin allah, kana zaune a tsakiyar tekuna,To, kai mutum ne kawai, ba allah ba,Ko da yake ka aza kanka mai hikima ne kamar Allah.

3. Lalle ka fi Daniyel hikima,Ba asirin da yake ɓoye a gare ka.

4. Ta wurin hikimarka da ganewarka ka samo wa kanka dukiya,Ka tattara zinariya da azurfa a baitulmalinka.

Karanta cikakken babi Ez 28