Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 26:15-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Ubangiji Allah ya ce wa Taya, “Sa'ad da kika fāɗi, ƙasashen da suke a gāɓar teku za su girgiza saboda amon fāɗuwarki, da nishin waɗanda ake yi wa rauni, da kashe-kashen da aka yi a cikinki.

16. Sa'an nan sarakunan bakin teku za su sauka daga gadajen sarautarsu, su tuɓe rigunansu, da rigunansu waɗanda aka yi wa ado. Za su zauna a ƙasa suna rawar jiki a kowane lokaci. Za su razana saboda abin da ya same ki.

17. Za su yi makoki saboda ke, su ce,‘Ke wadda ake zaune cikinki, kin bace daga tekuna,Ya shahararren birni, wanda yake babba a bakin teku,Ke da mazaunan da suke cikinki, kun sa mazaunan gāɓar teku su ji tsoro!

Karanta cikakken babi Ez 26