Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 17:21-24 Littafi Mai Tsarki (HAU)

21. Dukan sojojinsa zaɓaɓɓu za a kashe su da takobi, za a watsar da waɗanda suka ragu ko'ina. Za ku sani ni Ubangiji ne na faɗa.”

22. Ga abin da Ubangiji Allah ya ce,“Ni kaina zan cire toho a kan itacen al'ul mai tsawo.Daga cikin sababbin rassansa zan karya lingaɓu,In dasa shi a tsauni mai tsayi.

23. A ƙwanƙolin tsaunin Isra'ila zan dasa shiDon ya fito da rassa, ya ba da 'ya'ya,Ya zama itacen al'ul na gaske.Tsuntsaye iri iri za su zauna a ƙarƙashinsa,Za su yi sheƙuna a cikin inuwar rassansa.

24. Dukan itatuwan jeji za su sani,Ni Ubangiji nakan sa manyan itatuwa su zama ƙanana,In sa ƙanana kuma su zama manya,In sa ɗanyen itace ya bushe,In sa busasshen itace kuma ya zama ɗanye, Ni Ubangiji na faɗa, zan kuwa aikata.”

Karanta cikakken babi Ez 17