Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 16:50-57 Littafi Mai Tsarki (HAU)

50. Su masu alfarma ne, sun aikata abubuwa masu banƙyama a gabana, saboda haka na kawar da su sa'ad da na gani.

51. “Samariya ba ta aikata rabin zunubin da kika aikata ba. Abubuwan banƙyama da kika aikata sun sa 'yan'uwanki sun zama kamar adalai.

52. Ke kuma sai ki sha kunyarki, gama kin sa 'yan'uwanki mata su sami rangwamin shari'a saboda zunubanki da kika aikata fiye da nasu, gama gwamma su da ke. Sai ki ji kunya, ki sha ƙasƙancinki, gama kin sa 'yan'uwanki mata su zama kamar adalai.”

53. Ubangiji ya ce wa Urushalima, “Zan komo da Saduma da Samariya da 'ya'yansu mata daga bauta. Sa'an nan zan komo da ke daga bauta tare da su,

54. don ki sha ƙasƙanci saboda abin kunyar da kika aikata. Ƙasƙancinki zai ta'azantar da 'yan'uwanki mata.

55. 'Yan'uwanki mata, wato Saduma da 'ya'yanta mata za su koma kamar yadda suke a dā, Samariya kuma da 'ya'yanta mata za su koma kamar yadda suke a dā. Ke kuma da 'ya'yanki mata za ku koma kamar yadda kuke a dā.

56. Ashe, ba ƙanwarki, Saduma, ta zama abar karin magana a bakinki a kwanakin fariyarki,

57. kafin asirin muguntarki ya tonu ba? Amma yanzu kin zama abin zargi ga 'ya'yan Edom mata, da waɗanda suke kewaye da ita, da 'ya'yan Filistiyawa mata waɗanda suke kewaye, waɗanda suke raina ki.

Karanta cikakken babi Ez 16