Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 11:1-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sai Ruhu ya ɗaga ni sama, ya kai ni ƙofar gabas ta Haikalin Ubangiji wadda dake fuskantar gabas. Sai ga mutum ashirin da biyar a bakin ƙofar. A cikinsu na ga Yazaniya ɗan Azzur, da Felatiya ɗan Benaiya, shugabannin jama'a.

2. Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan su ne mutanen da suke ƙulla mugunta, waɗanda suke ba da muguwar shawara a cikin birnin.

3. Waɗanda suke cewa, ‘Lokacin gina gidaje bai yi kusa ba. Wannan birni tukunya ce mai ɓararraka, mu ne kuwa naman.’

4. Saboda haka ka yi musu annabci marar kyau, ka yi annabci, ya ɗan mutum!”

5. Sa'an nan Ruhun Ubangiji ya sauko a kaina, ya ce mini, “Ka ce, ‘In ji Ubangiji, haka kuke tunani, ku mutanen Isra'ila, gama na san abin da yake cikin zuciyarku.

6. Kun kashe mutane da yawa a wannan birni, har kun cika titunansa da gawawwaki.’

Karanta cikakken babi Ez 11