12. Yana da ganyaye masu kyauDa 'ya'ya jingim don kowa da kowa ya ci.Namomin jeji suka sami inuwa a ƙarƙashinsa,Tsuntsayen sama kuma suka zauna a rassansa.Dukan masu rai a gare shi suka sami abinci.
13. “ ‘A cikin wahayin da na gani sa'ad da nake kwance a gado, sai ga wani mai tsaro, tsattsarka, ya sauko daga sama.
14. Sai ya yi magana da ƙarfi, ya ce,“A sare itacen, a daddatse rassansa,A zage ganyayensa ƙaƙaf, a warwatsar da 'ya'yansa.A sa namomin jeji su gudu daga ƙarƙashinsa,Tsuntsaye kuma su tashi daga rassansa.
15. Amma a bar kututturen da saiwoyinsa a ƙasaƊaure da sarƙar baƙin ƙarfe da tagulla.A bar shi can cikin ɗanyar ciyawar saura,Ya jiƙe da raɓa,Ya yi ta cin ciyawa tare da namomin jeji.
16. A raba shi da hankali irin na mutane,A ba shi irin na dabba.Zai zauna a wannan hali har shekara bakwai.