Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Dan 4:1-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. “Daga sarki Nebukadnezzar zuwa ga dukan mutane, da al'ummai, da harsuna mabambanta waɗanda suke zaune a duniya duka. Salama mai yawa ta tabbata a gare ku!

2. Na ga ya yi kyau in sanar muku da alamu da abubuwan al'ajabi waɗanda Allah Maɗaukaki ya nuna mini.

3. “Alamunsa da girma suke!Al'ajabansa da bantsoro suke!Sarautarsa ta har abada ce,Mulkinsa kuma daga zamani zuwa zamani ne.

4. “Ni, Nebukadnezzar ina cikin gidana, ina nishaɗi a fādata.

5. Sa'ad da nake kwance a gādona, sai na yi mafarki wanda ya tsorata ni. Tunanina da wahayi suka firgitar da ni.

6. Don haka na umarta a kirawo mini dukan masu hikima na Babila don su yi mini fassarar mafarkin.

7. Sai masu sihiri, da masu dabo, da Kaldiyawa, da masu duba suka zo, na faɗa musu mafarkin, amma ba su iya yi mini fassararsa ba.

8. Daga baya sai Daniyel wanda aka laƙaba wa suna Belteshazzar, wato irin sunan allahna, yana kuwa da ruhun alloli tsarkaka, ya shigo wurina. Na kuwa faɗa masa mafarkin, na ce,

9. ‘Ya Belteshazzar shugaban masu sihiri, tun da yake na san ruhun alloli tsarkaka yana a cikinka, ba wani asirin da zai fi ƙarfin ganewarka. Ga mafarkin da na yi, sai ka faɗa mini fassararsa.

10. “ ‘Wahayin da na gani ke nan sa'ad da nake kwance a gadona. Na ga wani itace mai tsayi ƙwarai a tsakiyar duniya.

Karanta cikakken babi Dan 4