Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Dan 2:19-26 Littafi Mai Tsarki (HAU)

19. Sai aka bayyana wa Daniyel asirin ta cikin wahayi da dare. Daga nan Daniyel ya yabi Allah na Sama.

20. Ya ce,“Yabo ya tabbata ga sunan Allah har abada abadin,Wanda hikima da iko nasa ne.

21. Yana da ikon sāke lokatai,Yakan tuɓe sarakuna, ya kuma naɗa waɗansu.Yana ba masu hikima hikima, masu ilimi kuwa fahimi,

22. Yana bayyana zurfafan abubuwa masu wuyar ganewa,Ya san abin da yake cikin duhu.Haske kuma yana zaune tare da shi.

23. A gare ka nake ba da godiya da yabo, ya Allah na kakannina,Gama ka ba ni hikima da iko,Har ka sanar mini da abin da muka roƙe ka,Ka sanar mana da matsalar da ta dami sarki.”

24. Sa'an nan Daniyel ya tafi wurin Ariyok wanda sarki ya sa ya karkashe masu hikima na Babila, ya ce masa, “Kada ka karkashe masu hikima na Babila, ka kai ni gaban sarki, ni kuwa zan yi wa sarki fassarar.”

25. Nan da nan kuwa Ariyok ya kai Daniyel gaban sarki, ya ce masa, “Na sami wani daga cikin kamammun ƙasar Yahuza wanda zai iya sanar wa sarki da fassarar.”

26. Sarki kuwa ya ce wa Daniyel, mai suna Belteshazzar, “Ka iya faɗa mini mafarkin duk da fassararsa?”

Karanta cikakken babi Dan 2