Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Tar 9:1-3 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sa'ad da Sarauniyar Sheba ta ji labarin irin suna da Sulemanu ya yi, sai ta zo Urushalima don ta jarraba shi da tambayoyi masu wuya. Ta zo da 'yan rakiya masu yawa, da raƙuma ɗauke da kayan yaji, da zinariya mai yawa, da duwatsu masu daraja. Sa'ad da ta zo wurin Sulemanu, ta faɗa masa dukan abin da yake a ranta.

2. Sulemanu kuwa ya amsa dukan tambayoyin da ta yi masa, ba wani abu da yake ɓoye ga Sulemanu wanda ya kāsa bayyana mata.

3. Sa'ad da Sarauniyar Sheba ta ga hikimar Sulemanu, da gidan da ya gina,

Karanta cikakken babi 2 Tar 9