Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Sar 4:11-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

11. Wata rana da Elisha ya zo, ya shiga ɗakin, ya huta.

12. Sai ya ce wa baransa, Gehazi, “Kirawo matan nan.” Da ya kirawo ta, sai ta zo ta tsaya a gabansa.

13. Ya ce wa Gehazi, “Ka tambaye ta me take so in yi mata saboda dukan wannan wahala da ta yi dominmu? Tana so in yi mata magana da sarki ko da shugaban sojoji?”Sai ta ce, “Ai, ina da dukan abin da nake bukata a cikin jama'ata.”

14. Elisha ya ce, “To, me za a yi mata?”Sai Gehazi ya amsa ya ce, “Ai, ba ta da ɗa, mijinta kuwa tsoho ne.”

15. Sai ya ce, “Kirawo ta.” Da ya kirawo ta, sai ta zo ta tsaya a ƙofar ɗakin.

16. Elisha kuwa ya ce mata, “Baɗi war haka za ki rungumi ɗa na kanki.”Sai ta ce, “A'a, ya shugabana, mutumin Allah, kada fa ka yi mini ƙarya.”

17. Amma macen ta sami juna biyu, ta kuwa haifi ɗa a daidai lokacin da Elisha ya faɗa mata.

18. Da yaron ya yi girma, sai wata rana ya bi mahaifinsa gona zuwa wurin masu girbi.

19. Sai ya ce wa mahaifinsa, “Wayyo, kaina, kaina.”Uban kuwa ya ce wa baransa, “Ka ɗauke shi, ka kai shi wurin uwar.”

Karanta cikakken babi 2 Sar 4