Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Sar 1:4-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. Ku faɗa wa sarki, Ubangiji ya ce, ‘Ba za ka tashi daga kan gadon da kake kwance ba, amma lalle za ka mutu.’ ”Iliya ya yi kamar yadda Ubangiji ya umarce shi, sai ya tafi.

5. Manzannin kuwa suka koma wurin sarki. Sarki ya ce, “Me ya sa kuka komo?”

6. Suka ce masa, “Wani mutum ya sadu da mu, ya ce mana, mu koma wurinka mu shaida maka, ‘Ubangiji ya ce, ba Allah a Isra'ila, har aka aike ku ku tambayi Ba'alzabul, gunkin Ekron? Domin haka ba za ka tashi daga kan gadon da kake kwance ba, amma lalle za ka mutu.’ ”

Karanta cikakken babi 2 Sar 1