Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Sam 12:1-3 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sai Ubangiji ya aiki Natan wurin Dawuda. Ya je wurinsa ya ce masa, “Akwai waɗansu mutum biyu a cikin wani gari. Ɗayan basarake ne, attajiri, ɗayan kuwa talaka ne, matalauci.

2. Basaraken yana da garkunan tumaki, da na awaki, da na shanu.

3. Amma talakan ba shi da kome sai 'yar tunkiyar da ya sayo. Ya yi renonta, ta yi girma a wurinsa, tare da 'ya'yansa. Takan ci daga cikin ɗan abincinsa, ta kuma sha daga cikin abin shansa, ta kwanta a ƙirjinsa. Ta zama kamar 'ya a gare shi.

Karanta cikakken babi 2 Sam 12