Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Tar 2:16-25 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. 'Yan'uwansu mata kuwa su ne Zeruya da Abigail.'Ya'yan Zeruya, maza, su ne Abishai, da Yowab, da Asahel, su uku ke nan.

17. Abigail ta haifi Amasa. Mahaifin Amasa shi ne Yeter daga zuriyar Isma'ilu.

18. Azuba, matar Kalibu ɗan Hesruna ta haifa masa 'ya'ya maza. Matarsa Yeriyot kuma ta haifi 'ya'ya maza, su ne Yesher, da Shobab, da Ardon.

19. Sa'ad da Azuba ta rasu sai Kalibu ya auri Efrata wadda ta haifa masa Hur.

20. Hur shi ne mahaifin Uri, Uri kuwa shi ne mahaifin Bezalel.

21. Bayan haka sai Hesruna ya shiga wurin 'yar Makir mahaifin Gileyad, wadda ya aura sa'ad da yake da shekara sittin da haihuwa. Ta haifa masa Segub.

22. Segub shi ne mahaifin Yayir wanda yake da birane ashirin da uku a ƙasar Gileyad.

23. Amma sai Geshur da Aram suka ƙwace garuruwan Hawwotyayir ɗin daga gare su, har da Kenat da ƙauyukanta, garuruwa sittin. Duk waɗannan su ne zuriyar Makir mahaifin Gileyad.

24. Bayan rasuwar Hesruna, Abaija, matarsa, ta haifa masa Ashur, mahaifin Tekowa.

25. 'Ya'yan Yerameyel ɗan farin Hesruna, su ne Arama ɗan fari, sa'an nan Buna, da Oren, da Ozem, da Ahaija.

Karanta cikakken babi 1 Tar 2