Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Tar 10:1-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra'ilawa, Isra'ilawa suka gudu a gaban Filistiyawa, aka karkashe su a Dutsen Gilbowa.

2. Filistiyawa suka kama Saul da 'ya'yansa maza, suka kashe Jonatan da Yishwi, da Malkishuwa.

3. Yaƙin ya tsananta wa Saul, maharba suka rutsa Saul, suka yi masa rauni.

4. Sai Saul ya ce wa mai ɗaukar makamansa, “Zare takobinka, ka kashe ni, don kada marasa kaciyan nan su zo su yi mini ba'a.” Amma mai ɗaukar makamai nasa bai yarda ba, gama yana jin tsoro ƙwarai. Saboda haka sai Saul ya zare takobinsa ya fāɗi a kansa.

5. Sa'ad da mai ɗaukar makamansa ya ga Saul ya mutu, sai shi ma ya faɗi a kan takobinsa ya mutu.

6. Ta haka Saul ya mutu, shi da 'ya'yansa maza guda uku tare da dukan gidansa.

Karanta cikakken babi 1 Tar 10