Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Sar 2:12-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

12. Sulemanu kuwa ya hau gadon sarautar ubansa, Dawuda. Mulkinsa kuma ya kahu sosai.

13. Sa'an nan Adonija ɗan Haggit ya tafi wurin Bat-sheba, tsohuwar Sulemanu. Ta ce masa, “Ka zo lafiya?”Ya ce, “Lafiya lau.”

14. Sa'an nan ya ce, “Ina da wani abin da zan faɗa miki.”Ta ce, “To, sai ka faɗa.”

15. Ya amsa ya ce, “Kin sani dai sarauta tawa ce. Ni ne kuwa mutanen Isra'ila duka suka sa zuciya zan ci sarautar, amma al'amarin ya sāke, sai sarautar ta zama ta ƙanena , gama tasa ce bisa ga nufin Allah.

16. Yanzu dai ina da roƙo guda zuwa gare ki, kada ki hana mini.”

17. Ta ce masa, “To, sai ka faɗa.”Sai ya ce, “In kin yarda ki yi magana da sarki Sulemanu, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce ya ba ni yarinyar nan, Abishag, daga Shunem, ta zama matata.”

Karanta cikakken babi 1 Sar 2