Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Sam 25:36-39 Littafi Mai Tsarki (HAU)

36. Abigail ta koma wurin Nabal, ta iske shi yana biki irin na sarakuna a gidansa. Ya yi ta nishaɗi, ya bugu sosai, don haka ba ta ce masa kome ba sai da safe.

37. Da safe, sa'ad da ruwan inabi ya sake shi, sai Abigail ta faɗa masa abin da ya faru. Zuciyarsa kuwa ta tsinke gaba ɗaya.

38. Bayan kwana goma sai Ubangiji ya bugi Nabal, ya mutu.

39. Sa'ad da Dawuda ya ji Nabal ya mutu, sai ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji wanda ya sāka mini a kan irin rainin da Nabal ya yi mini. Ya kuma hana ni aikata mugunta. Ya ɗora wa Nabal muguntarsa a kansa.”Sa'an nan Dawuda ya aika, ya nemi Abigail ta zama matarsa.

Karanta cikakken babi 1 Sam 25