Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Sam 17:55-58 Littafi Mai Tsarki (HAU)

55. Sa'ad da Saul ya ga Dawuda ya tafi ya yi yaƙi da Goliyat, ya ce wa Abner, sarkin yaƙinsa, “Abner, ɗan wane ne wannan saurayi?”Abner ya amsa, ya ce, “Ranka ya daɗe, ya sarki, ban sani ba.”

56. Sai ya ce, “Ka tambaya mini, wane ne uban saurayin nan.”

57. Da Dawuda ya komo daga kisan Goliyat, sai Abner ya kai shi wurin Saul, Dawuda yana ɗauke da kan Bafilisten.

58. Saul ya tambayi Dawuda, ya ce, “Saurayi, kai ɗan wane ne?”Dawuda ya amsa, ya ce, “Ni ɗan baranka ne, Yesse, mutumin Baitalami.”

Karanta cikakken babi 1 Sam 17