Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Sam 17:1-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sai Filistiyawa suka tattaru a Soko ta Yahuza, suka kafa sansani a tsakanin Soko da Azeka, a Efes-dammim.

2. Saul kuma da mutanen Isra'ila suka tattaru, suka kafa sansani a kwarin Ila, suka jā dāga don su yi yaƙi da Filistiyawa.

3. Filistiyawa suka jeru a tudu guda, Isra'ilawa kuwa a ɗaya tudun. Kwari yana tsakaninsu.

4. Akwai wani jarumi, sunansa Goliyat, ya fito daga sansanin Filistiyawa. Tsayinsa kamu shida da rabi.

5. Yana sa kwalkwali na tagulla a kansa, yana kuma saye da sulke na tagulla wanda nauyinsa ya fi shekel dubu biyar (5,000).

6. Ya sa safa ta tagulla a ƙafafunsa, yana kuma da mashi na tagulla saɓe a kafaɗarsa.

7. Gorar mashinsa ta yi kama da dirkar masaƙa. Nauyin ruwan mashinsa na baƙin ƙarfe shekel ɗari shida ne. Mai ɗaukar masa garkuwa yana tafe a gabansa.

8. Goliyat ya ta da murya da ƙarfi, ya yi kira ga rundunar Isra'ila, ya ce, “Don me kuka fito ku jā dāgar yaƙi? Ai, ni Bafiliste ne, ku kuwa barorin Saul! Ku zaɓi mutum guda daga cikinku ya gangaro nan wurina.

Karanta cikakken babi 1 Sam 17