Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Sam 10:18-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. Ya ce musu, “In ji Ubangiji Allah na Isra'ila, ‘Ni na fito da Isra'ilawa daga Masar, na cece ku daga Masarawa da kuma daga hannun mulkokin da suka wahalshe ku.

19. Ni ne Allahnku wanda yake cetonku daga dukan masifu da wahalai, amma ga shi yau, kun ƙi ni kuna roƙona in ba ku sarki. To, da kyau, yanzu fa sai ku kusato gaban Ubangiji kabila kabila da iyali iyali.’ ”

20. Sa'an nan Sama'ila ya ce wa kabilan Isra'ila su guso, kuri'a kuwa ta faɗa a kan kabilar Biliyaminu.

21. Sai kuma ya sa kabilar Biliyaminu ta guso iyali iyali, kuri'a kuwa ta faɗa a kan iyalin Matri. Sa'an nan kuma ya guso da iyalin Matri mutum mutum, kuri'a ta faɗa a kan Saul, ɗan Kish. Amma sa'ad da suka neme shi, ba a same shi ba.

22. Suka yi tambaya a wurin Ubangiji, suka ce, “Ko akwai wani dabam?”Ubangiji ya ce, “Ai, ga shi can, ya ɓuya cikin kayayyaki.”

23. Sai suka sheƙa, suka fito da shi daga wurin da ya ɓuya, ya tsaya cikin mutane, ya fi kowa tsayi da misalin ƙafa guda.

Karanta cikakken babi 1 Sam 10