Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Sam 10:14-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

14. Kawun Saul kuwa ya tambaye shi, shi da baransa, “Ina ne kuka tafi?”Saul ya ce, “Mun je neman jakuna, da ba mu same su ba, sai muka tafi wurin Sama'ila.”

15. Kawunsa kuma ya ce, “In ka yarda ka faɗa mini abin da Sama'ila ya faɗa maka.”

16. Saul kuwa ya ce wa kawunsa, “Ya faɗa mana a fili an gane jakunan.” Amma bai faɗa wa kawunsa zancen sarautar da Sama'ila ya faɗa masa ba.

17. Sama'ila kuwa ya tara mutanen Isra'ila a gaban Ubangiji a Mizfa.

18. Ya ce musu, “In ji Ubangiji Allah na Isra'ila, ‘Ni na fito da Isra'ilawa daga Masar, na cece ku daga Masarawa da kuma daga hannun mulkokin da suka wahalshe ku.

19. Ni ne Allahnku wanda yake cetonku daga dukan masifu da wahalai, amma ga shi yau, kun ƙi ni kuna roƙona in ba ku sarki. To, da kyau, yanzu fa sai ku kusato gaban Ubangiji kabila kabila da iyali iyali.’ ”

20. Sa'an nan Sama'ila ya ce wa kabilan Isra'ila su guso, kuri'a kuwa ta faɗa a kan kabilar Biliyaminu.

Karanta cikakken babi 1 Sam 10