Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 8:12-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

12. Sai Yesu ya ƙara musu da cewa, “Ni ne Hasken duniya. Wanda yake bi na ba zai yi tafiya a duhu ba, amma zai sami hasken rai,”

13. Saboda haka Farisiyawa suka ce masa, “Kanka kake wa shaida, shaidarka kuwa ba tabbatacciya ba ce.”

14. Yesu ya amsa musu ya ce, “Ko na shaidi kaina, ai, shaidata tabbatacciya ce, domin na san inda na fito, da kuma inda za ni. Amma ku ba ku san inda na fito ba, ko kuma inda za ni.

15. Ku kuna hukunci irin na duniya ne, ni kuwa ba na hukunta kowa.

16. Amma ko da zan yi hukunci, hukuncina na gaskiya ne, domin ba ni kaɗai nake ba, ni da Uba wanda ya aiko ni ne.

17. A Attaurarku ma a rubuce yake, cewa shaidar mutum biyu tabbatacciya ce.

18. Ni ne nake shaidar kaina, Uba da ya aiko ni kuma yana shaidata.”

Karanta cikakken babi Yah 8