Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Rom 9:17-31 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Don a Nassi an ce da Fir'auna, “Na girmama ka ne musamman, domin in nuna ikona a kanka, domin kuma a sanar da sunana a duniya duka.”

18. Wato, yana nuna jinƙai ga wanda ya so, yana kuma taurara zuciyar wanda ya so.

19. Kila ka ce mini, “To, don me har yanzu yake ganin laifi? Wa zai iya tsayayya da nufinsa?”

20. Ya kai ɗan adam! Wane ne kai har da za ka yi jayayya da Allah? Ashe, abin da aka gina zai iya ce wa magininsa, “Don me ka yi ni haka?”

21. Ashe, maginin tukwane ba ya iko da yumɓu, ya gina wata domin aiki mai martaba, wata kuma don kasasshen aiki, duk daga curi ɗaya?

22. To, ƙaƙa fa? Allah da yake yana so ya nuna fushinsa, ya kuma bayyana ikonsa, sai ya haƙura matuƙar haƙuri da waɗanda suka cancanci fushinsa, suka kuma isa hallaka,

23. Nufinsa ne yă bayyana yalwar ɗaukakarsa ga waɗanda ya yi wa jinƙai, wato, waɗanda dā ma ya yi wa tanadin ɗaukaka?

24. Wato, mu ke nan da ya kira, ba kuwa daga cikin Yahudawa kaɗai ba, har ma daga cikin al'ummai.

25. Kamar dai yadda ya faɗa a Littafin Yusha'u cewa,“Waɗanda dā ba jama'ata ba,Zan ce da su ‘jama'ata,’Wadda dā ba abar ƙaunata ba kuma,Zan ce da ita ‘abar ƙaunata.’ ”

26. “A daidai wurin da aka ce da su, ‘Ku ba jama'ata ba ne,’A nan ne za a kira su ‘'ya'yan Allah Rayayye,’ ”

27. A game da Isra'ila Ishaya ma ya ɗaga murya ya ce, “Ko da yake yawan Isra'ilawa ya kai kamar yashin teku, duk da haka kaɗan ne za su sami ceto.

28. Domin Ubangiji zai zartar da hukuncinsa a duniya, ya gama shi tashi ɗaya.”

29. Kamar yadda Ishaya ya yi faɗa cewa,“Da ba domin Ubangijin Runduna ya bar mana zuriya ba,Da mun zama kamar Saduma,An kuma maishe mu kamar Gwamrata.”

30. To, me kuma za mu ce? Ga shi, al'ummai da ba su nace da neman adalcin Allah ba, sun samu, wato, sun sami adalcin da yake daga bangaskiya.

31. Isra'ila kuwa da suka nace da neman hanyar adalcin Allah, suka kasa samunta.

Karanta cikakken babi Rom 9