Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mat 17:7-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Sai Yesu ya zo ya taɓa su, ya ce, “Ku tashi, kada ku ji tsoro.”

8. Da suka ɗaga kai ba su ga kowa ba, sai Yesu kaɗai.

9. Suna cikin gangarowa daga dutsen, sai Yesu ya kwaɓe su ya ce, “Kada ku gaya wa kowa abin da kuka gani, sai an ta da Ɗan Mutum daga matattu.”

10. Almajiran suka tambaye shi suka ce, “To, yaya malaman Attaura suke cewa, lalle ne Iliya ya riga zuwa?”

11. Ya amsa ya ce, “Lalle Iliya zai zo ne, zai kuwa raya dukan abubuwa.

12. Amma ina gaya muku, Iliya ya riga ya zo, ba su kuwa san shi ne ba, har ma suka yi masa abin da suka ga dama. Haka kuma Ɗan Mutum zai sha wuya a hannunsu.”

13. Sa'an nan ne almajiran suka gane, ashe, zancen Yahaya Maibaftisma yake yi musu.

14. Da suka isa wurin taro, sai wani mutum ya zo gare shi, ya durƙusa a gabansa, ya ce,

15. “Ya Ubangiji, ka ji tausayin ɗana, yana farfaɗiya, yana shan wuya ƙwarai, sau da yawa yakan faɗa wuta da kuma ruwa.

16. Na kuwa kai shi wurin almajiranka, amma ba su iya warkar da shi ba.”

17. Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ya ku marasa bangaskiya, kangararru na wannan zamani! Har yaushe zan zama da ku? Har yaushe kuma zan jure muku? Ku kawo mini shi nan.”

18. Sai Yesu ya tsawata masa, aljanin kuma ya rabu da shi. Nan take yaron ya warke.

19. Sa'an nan almajiran suka zo wurin Yesu a keɓe, suka ce, “Me ya sa mu muka kasa fitar da shi?

20. Ya ce musu, “Saboda ƙarancin bangaskiyarku. Domin hakika ina gaya muku, da kuna da bangaskiya, ko misalin ƙwayar mustad, da za ku ce wa dutsen nan, ‘Kawu daga nan, ka koma can!’, sai kuwa ya kawu. Ba kuwa abin da zai gagare ku. [

Karanta cikakken babi Mat 17