Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 7:13-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Ta haka kuke banzanta Maganar Allah ta wajen al'adunku na gargajiya. Kun kuwa cika yin irin waɗannan abubuwa.”

14. Sai ya sāke kiran jama'a, yă ce musu, “Ku saurare ni dukanku, ku kuma fahimta.

15. Ba abin da yake shiga mutum daga waje yă ƙazanta shi, sai abin da yake fita, yake ƙazanta shi. [

16. Duk mai kunnen ji, yă ji.]”

17. Bayan rabuwarsa da taron, da ya shiga gida, almajiransa suka tambaye shi ma'anar misalin.

18. Ya ce musu, “Ashe, ku ma ba ku da fahimta ne? Ashe, ba ku gane ba, kome ya shiga mutum daga waje, ba yadda zai ƙazanta shi,

19. tun da yake ba zuciya tasa ya shiga ba, cikinsa ne, ta haka kuma zai fita?” Ta haka Yesu ya halatta kowane irin abinci.

20. Ya kuma ce, “Abin da yake fita daga cikin mutum yake ƙazanta shi.

21. Don daga ciki ne, wato daga zuciyar mutum, mugayen tunani yake fitowa, kamar su fasikanci, da sata, da kisankai, da zina,

22. da kwaɗayi, da mugunta, da ha'inci, da fajirci, da kishi, da yanke, da girmankai, da kuma wauta.

23. Duk waɗannan mugayen abubuwa daga ciki suke fitowa, suna kuwa ƙazanta mutum.”

Karanta cikakken babi Mar 7