Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 4:5-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Waɗansu kuma suka faɗa a wuri mai duwatsu inda ba ƙasa da yawa. Nan da nan kuwa suka tsiro saboda rashin zurfin ƙasa.

6. Da rana fa ta ɗaga, sai suka yanƙwane, da yake ba su da saiwa sosai, suka bushe.

7. Waɗansu kuma suka faɗa cikin ƙaya, sai ƙayar ta tashi ta sarƙe su, ba su yi tsaba ba.

8. Waɗansu kuma suka faɗa a ƙasa mai kyau, suka yi yabanya, suka girma, suka yi tsaba, waɗansu riɓi talatin talatin, waɗansu sittin sittin, waɗansu ma har ɗari ɗari.”

9. Sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”

10. Da suka kaɗaita, masu binsa da su sha biyun nan suka tambaye shi ma'anar misalan.

11. Sai ya ce musu, “Ku kam, an yardar muku ku san asirin Mulkin Allah, amma ga waɗanda ba sa cikinku, kome sai a cikin misali,

Karanta cikakken babi Mar 4