Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 24:12-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

12. Amma Bitrus ya tashi, ya doshi kabarin da gudu. Ya duƙa, ya leƙa a ciki, ya ga likkafanin lilin a ajiye waje ɗaya. Sai ya koma gida yana al'ajabin abin da ya auku.

13. A ran nan kuma sai ga waɗansu biyu suna tafiya wani ƙauye, mai suna Imuwasu, nisansa daga Urushalima kuwa kusan mil bakwai ne.

14. Suna ta zance da juna a kan dukan al'amuran da suka faru.

15. Ya zamana tun suna magana, suna tunani tare, sai Yesu da kansa ya matso, suka tafi tare.

Karanta cikakken babi Luk 24